fidelitybank

An tono gawar wani Almajiri bayan an binne shi a Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano, ta bayar da umarnin tono gawar wani almajiri wanda ake zargin malaminsa ya halaka shi ta hanyar duka.

Kwamishinan Harkokin Addinai Dr. Muhammad Tahar Adamu (Baba Impossible) ne ya bayyana hakan yayin da ya jagoranci bankado makarantar ’yan marin da ke unguwar Wailari a yankin Na’ibawa.

Aminiya ta rawaito cewa, ana zargin malamin da yi wa almajirin dukan kawo wuka, lamarin da ya yi ajalinsa.

Haka kuma rahotanni sun bayyana cewa lokacin da almajirin ya rasu ba a sanar da iyayensa ba aka je aka binne shi.

Baba Impossible ya bayyana cewa, gwamnatin ta sa ’yan sanda su hako gawar almajirin tare da gudanar da bincike, domin gano musabbabin rasuwarsa.

Da yake nasa jawabin, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa a yanzu haka mai makarantar da sauran wadanda ke taimaka masa suna hannu, domin fadada bincike a kai tare da rufe makarantar.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp