fidelitybank

‘Yan sanda sun gayyaci tsohon kwamishinan gwamnatin Ganduje

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta gayyaci tsohon kwamishinan ayyuka a gwamnatin gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Muazu Magaji.

Da ya ke zantawa da Aminiya, Magaji ya ce, ofishin siyasa na hukumar SBI ne ya gayyace shi, amma ba su bayyana masa mene ne makasudin gayyatar ba.

“Na sami waya cewa suna son in bayyana a gabansu. Na tambaye su a kan menene ? kuma suka ce min zan san duk abubuwan da ke faruwa idan na zo.

“Lokacin da na je sai suka ce, gwamnatin jihar Kano ce ta kai kara ta,” inji shi.Da aka tambaye shi ko ya mutunta gayyatar? Tsohon kwamishinan ya ce, “A yanzu haka ina Abuja, kuma zan mutunta gayyatar da zarar na isa Kano a ranar Talata.

“Me nake gudu? Tabbas zan girmama gayyatar gobe,” ya tabbatar.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa bai samu, cewa uffan ba game da lamarin.

Magaji dai ya sha cece-kuce tun bayan da aka kore shi daga mukamin kwamishinan ayyuka.

Gwamnan ya sa ke nada shi a matsayin mai taimaka masa kan bututun iskar gas na AKK, amma ya kore shi daga baya.

Tun daga wancan lokacin tsohon kwamishinan da aka kora ya rinka sukar Ganduje da gwamnatinsa a Facebook.

A halin yanzu, Magaji dan tsagin Shekarau ne na jam’iyyar APC.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp