Rundunar ’yan sandan jihar Kaduna, ta tabbatar da yin garkuwa da wata mata da ‘ya’yan ta hudu da a ka yi garkuwa da su a jihar Kaduna.
Mai magana da yawun runduanr, ASP, Jalige Mohammed ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.
Ya ce,”Lamarin ya faru ne a karamar hukumar Chikun a jihar, sakamakon kira da mu ka samu daga unguwar Sabo GRA a lokacin da su ke kokarin neman kutsawa gidan, inda wasu masu garkuwa da mutane su ka yi dirar mikiya a gidan matar suka tafi da ita da ’ya’yanta ne a unguwar Sabon Tasha kafin wayewar garin ranar Asabar. Kuma za mu yi kokari wajen ganin mun kubutar da su cikin aminci”, inji ASP Jalige.