Taurarin fina-finan Kannywood sun bi sahun sauran mutane a Najeriya wajen caccakar gwamnatin Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, saboda zargin gazawarta wajen tabbatar da tsaro a Arewacin Najeriya.
Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan wasu ‘yan bindiga su ka kai hari kan fasinjojin da suka fito daga karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sokoto, domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan, saboda ta’azzarar hare-haren ‘yan bindiga.
Bayanai sun nuna cewa ‘yan bindigar sun banka wuta kan motar da mutanen akalla 40 suke ciki inda suka kone kurmus.
Wani ganau ya gaya wa BBC cewa: “Lokacin da abin ya faru ina Sabon Birni aka kira ni aka shaida min. Daga cikin matafiyan ma har da wani ƙanin mahaifiyata da matarsa da ƴaƴansu huɗu”.