fidelitybank

‘Yan daba sun kai hari karamar hukumar Ezza a jihar Enugu

Date:

Wasu ’yan daba sun kai hari tare da kona shelkwatar karamar hukumar Ezza ta Arewa a jihar Ebonyi, gabanin zabe mai zuwa.

Rahotanni sun nuna cewa, hare-haren da kona karamar hukumar Ezza ta Arewa, ya zo ne daf da rantsar da sabon shugaban karamar hukumar a jihar.

Ku tuna cewa Nora Alo, tsohon shugaban karamar hukumar Ezza ta Arewa kuma ya mika wa sabon shugaban Mista Ogodo Ali Nomeh.

An tattaro cewa barayin sun kutsa cikin wasu ofisoshi, inda aka ajiye muhimman takardu suka kwashe su tare da kona wasu daga cikinsu.

Da yake tabbatar da faruwar harin, sabon shugaban karamar hukumar, Mista Ogodo Ali Nomeh, ya ce ‘yan ta’addan sun yi artabu da jami’an tsaron da ke kula da majalisar ne, kuma wasu daga cikin ‘yan bindigar sun samu raunuka a harbin bindiga.

Ya ce har yanzu ba a kama ‘yan ta’addan ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

A cewarsa: “Ba mu kama kowa ba a yanzu. Kun san abin ya faru da daddare kuma kafin mu fito da safen nan tuni suka tsere.

“Akwai harbin bindiga da yawa. Kuma ina tsammanin da yawa daga cikinsu sun ji rauni. Don haka, muna tafiya daga wannan asibiti zuwa wancan don duba mutanen da suka samu raunukan harbin bindiga.

“Ba mu zargin kowa a yanzu, har sai mun kama wadanda ake zargin. Kun san lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:00 na safe.

“Muna tattaunawa da jami’an tsaro da suka yi karo da ‘yan ta’addan,” in ji shi.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...
X whatsapp