Yan bindiga sun sako wasu mata ciki har da mata biyu na lakcaran Kwalejin Ilimi da fasaha dake Gusau a jihar Zamfara, Dr. Abdulrazak Mu’azu, bayan sun karbi kudin fansa.
Punch ta rawaito cewa wani daga cikin iyalan gidan malamin, Muhammed Bello, ya ce, ‘yan bindigan sun sako su ne da safiyar Litinin, bayan sun amince su karbi Naira miliyan 10 a matsayin fansa.
Da farko, bayan ‘yan bindiga sun sace iyalan malamin Kwalejin, sun nemi a biya Naira miliyan 50m a matsayin fansa, amma daga baya su ka daidai ta a kan Naira miliyan 10m.
Maharan sun sace matar malamin, mai suna Binta Jabaka, da ƴaƴansa mata biyu, Maryam Abdurrazak da Hafsat Abdurrazak, a gidansu da ke ƙauyen Mareri, kusa da garin Gusau, da tsakiyar dare ranar Jumu’a.