fidelitybank

‘Yan bindiga sun kwace wani yanki a Neja tare da karbar kudin haraji

Date:

Rahotanni sun ce ‘yan bindiga sun kwace iko da wasu yanki a jihar Neja, inda suka kafa kofofin karbar haraji tare da sanya haraji kan manoma da mazauna yankin.

Yankunan da abin ya shafa sun hada da Dogon-Dawa, Kurege, Kangarewa, Mangoro, da sauransu, inda aka ce ‘yan bindigar na gudanar da yankunan ne bisa ka’idojinsu.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan ta’addan sun sanya dokar hana zirga-zirgar kayayyaki da jama’a, lamarin da ya tilasta musu biyan haraji kafin tafiya.

A cewar shaidun gani da ido, a ranar Lahadin da ta gabata, an tilasta wa mazauna yankin biyan harajin Naira miliyan 3.5 kafin a bar motocin da ke dauke da kayansu su bar yankin.

‘Yan fashin dai ba su bar manoman ba, inda suka bukaci a biya su haraji kan amfanin gona da kuma tilasta musu biyan kafin a bar su su girbe amfanin gona.

Lamarin dai ya ta’azzara, har ta kai ga har ’yan gudun hijirar da ke neman ficewa daga yankin su biya takamammen haraji kafin tafiyarsu, kamar yadda shaidan ya yi zargin.

Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa ‘yan bindigar sun kirkiro yankin nasu ne, suna gudanar da ayyukansu ba tare da adawa ba.

Rahotanni sun bayyana cewa ana cajin motocin da ke barin yankin tsakanin Naira 200,000 zuwa Naira 300,000, inda aka tilasta wa hadakar motoci uku biyan Naira miliyan daya kafin a bar su su fita.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Neja, Wasiu Abiodun domin jin ta bakinsa kan lamarin, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike, kuma za a yi karin bayani.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp