fidelitybank

Yajin aikin ASUU ya shiga kwanaki 200

Date:

A ranar Juma’a ne aka cika kwanaki 200 cif, da fara yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’in Najeriya ASUU ta tsunduma.

A tsahon wannan lokacin dai an yi ta zama teburin sulhu tsakanin gwamnati da ASUU amma ana tashi ba tare da cimma matsaya ba.

Wasu daga cikin daliban da yajin aikin ya shafa, sun shaidawa BBC cewa ba su zaci lamarin zai kai tsahon wannan lokacin ba.

Daya daga cikinsu mai suna Ummi Musa, daliba a jami’ar Bayero da ke Kano ta ce: ”Muna tsaka da zana jarabawa aka tafi yajin aikin, daga farko gaskiya mun dan ji dadi, ganin cewa za mu samu karin makonni biyu na sake karatu.

Amma da aka wuce wannan lokacin sai muka gane shayi ruwa ne, lamarin nan ya janyoo mana cikas a karatu, musamman ni da ke shekara ta 4, a fannin shari’a.

Dan Allah gwamnati da ASUU su taimaka mana, saboda ni dai a yajin aiki aka haife ni, na girma acikinsa yau gashi har yazo kai na, idan tun daga wancan lokacin da malamai ke tafiya yajin aiki ba su yi galaba ba, kenan matakin ci gaba da yajin aiki ba zai sauya komai ba.”

Ita Shema’u ta shaidawa BBC saboda zaman gida da ya tura, har iyaye sun fara yi musu batun aure tun da karatun bai samu ba.

A watan Fabrairun 2022 ne dai malaman jami’o’in Najeriyar suka tafi yajin aiki, kan rashin biya musu bukatu da gwamnatin Najeriya ta yi da suka hada da alawus-alawus da karin albashi da sauransu.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp