Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya ce, gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi na da nagartar da zai iya doke tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar a takarar shugaban kasa a 2023.
A na dai kallon Atiku wanda ya sha kaye a zaben 2019 a hannun shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin wani babba mai karfi a fagen siyasa da za a iya fafatawa da shi a shekarar 2023 a jam’iyyar PDP.
Yayin da Yahaya Bello, wanda na jam’iyyar APC ne mai mulki ya nuna sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
Da ya ke magana a wata hira da gidan Talabijin na Channels, Fani-Kayode, wanda ya fice daga PDP zuwa APC a shekarar da ta gabata, ya bayyana Yahaya Bello a matsayin wanda ya fi Atiku dan takarar shugaban kasa nagarta.
“Na amince gwamna Yahaya Bello, shi ne wanda ya fi cancanta a matsayin shugaban Æ™asa, na yi amanna cewa, zai ja miliyoyin matasan Æ™asar nan, kuma shi ne sauyin wannan yanayin na mulki ga matasa kuma matashi”. In ji Kayode