Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, ‘Concerned Nigerians’, Deji Adeyanju, ya bayyana burin gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi a matsayin shugaban kasa ya na yaudara kan sa ne kawai.
PlatinumPost ta rawaito cewa, wasu kungiyoyi masu ruwa da tsaki sun yi ta yunƙurin ganin Yahaya Bello, ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC mai mulki a 2023, duk da hotunan yakin neman zabensa sun mamaye garuruwa da dama.
Yayin da gwamnan bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a hukumance ba, ya ci gaba da jaddada cewa, Najeriya na bukatar shugaban kasa na matasa kamar sa.
Dan gwagwarmayar a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook da aka tabbatar a ranar Asabar, wanda ya hada da hoton gwamnan da kuma tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya ce, Yahaya Bello zai rasa hatta kuri’un wakilan APC na Kogi a zaben fidda gwani na APC.