fidelitybank

Yadda kare ya cinyewa mai maganin gargajiya azzakari a Calabar

Date:

 

Wani mai maganin gargajiya, Ani Ikoneto ya rasa ransa bayan da karensa ya cire masa azzakari da ƴaƴan maraina ya kuma cinye su a ranar Kirsimeti.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, maƙwabtan Ikoneto, ɗan shekara 60 da yanke zaune a layin Jebbs da ke Calabar ta kudu sun baiyana cewa ya je ya shawu ne a ranar Kirsimeti inda ya dawo gida a buge.
Wani maƙwabcin mai maganin, mai suna Itoro, ya ce “mu mun riga mun kwanta amma wasu kuma sun ci gaba da hira a waje. Da ya dawo sai ya shiga dakinsa ya kwanta kuma bai rufe kofa ba. Da yana baccin, sai ya yi kashi.
“Shi kuma karen sai ya ji warin kashin sai ya sa karen ya shiga ɗakin nasa domin ya ci kashin. To da ya hau kan gadon, sai ya damƙi ƴaƴan marainan shi, ko ya zaci nama ne,” in ji Itoro.
Ya ƙara da cewa ihu da mai maganin ya yi ne ya ja hankalin mutanen da su ke zaune su na hira, inda su ka kai masa ɗauki su ka ga abin da ya faru.
“Mu na jin ihun sa sai mu ka zaci ko ƴan daba ne su ka kai masa hari, muna shiga sai mu ka duk jikin sa jini kuma da alamun gaban sa ya fice, sai mu ka shima karen duk bakin sa jini.
Itoro ya ƙara da cewa kafin su kai Ikoneto asibiti sai da su ka wawwanke masa jikin sa saboda kashi da jinin da ya ɓata shi.
Ya ce a lokacin da su ke gyara jikin nasa yana ta zubar da jini sosai inda kafin ma su karasa asibitin rai ya yi halinsa.
A washegarin Kirsimeti ne a ka kai shi ƙauyen su domin binnewa.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp