fidelitybank

Wike ya zargi Buhari da Amaechi da yin katsalandan a jihar sa

Date:

Gwamna Nyesom Wike ya zargi shugaban kasa Muhammadu Buhari da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da yin katsalandan a zaben gwamna na 2019 a jihar Ribas.

Gwamna Wike ya yi wannan ikirarin ne a ranar Larabar, yayin bikin kaddamar da aikin gina titunan cikin gida a garin Igwuruta da ke karamar hukumar Ikwerre ta jihar.

Ya ce shugaban kasar ta bakin tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya yi amfani da jami’an tsaro wajen yunkurin murde zaben gwamna.

Gwamnan ya ce al’ummar jihar sun yi watsi da matakin da hukumomin tsaro suka dauka.

Ya ce “Na ji Mista shugaban kasa ya fada jiya cewa, ba zai tsoma baki ba (a zaben 2023). Ya shaida wa gwamnonin ba zai tsoma baki ba.

“A daya (2019) kun tsoma baki tare da turo mutane su zo su karasa mu a jihar Ribas.

“Na gode shugaban kasa da cewa ba za ku tsoma baki ko tsoratar da kowa ba. Ma’ana babu wata hanya ga jam’iyyar ku.

“Tabbas ya tsoma baki a karon karshe ta hanyar amfani da sojoji ta hannun tsohon ministan sufuri amma jama’a suka tashi suka ce a’a hakan ba zai faru ba.

“Na gode wa shugaban kasa da ya ke son barin gadon gudanar da zabe na gaskiya da adalci”.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp