Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, ya gwangwaje wani gurgu, James Daniel, ɗalibin Jamia’r Jihar Rivers, RSU, da kuɗi, wuri na gugar wuri har naira miliyan 50.
Gwamnan bai tsaya a nan ba, sai kuma ya danƙawa shi wannan bawan Allah takardar ɗaukar aiki nan take, a matsayin lada na kammala digiri na uku, wanda a ka fi sani da digirin-digirgir, duk da cewa yana da nakasa a jikin sa.
Wike ya sanar da wannan tagomashi ne a jiya Asabar, a wajen bikin yaye ɗalibai karo na 33 a jami’ar, a garin Fatakwal.
Ya ce ya karrama Daniel ne saboda jajircewarsa wajen neman ilimi da kuma yadda ya zamto abin koyi ga mutane masu buƙata ta musamman.