Asusun tallafa wa yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya bayyana aniyar sa ga gwamnatin Najeriya na ƙara adadin kudin da ke kashewa kan ilimi da kashi hamsin cikin dari nan da shekara biyu masu zuwa.
Amma duk da wannan yunƙuri, Asusun ya ce, Najeriyar ta na da jan aiki a gabanta kafin ta kai mizanin kashi 15 zuwa 20 cikin 100 na kasafin kudin kowace kasa da MDD ta ce, ya kamata ta kebe wa ilimi.
Amma a cewar UNICEF, akwai aiki a gaban gwamnatin Najeriyar, kafin maganar ta zama faɗa da cikawa.
Asusun, a cikin wata sanarwa, ya yi la’akari da kasafin kudin Najeriyar na bana, wanda aka ƙiyasta zai ci Naira tiriliyan 17, an keɓe wa ilimi kashi bakwai da ƴar ɗoriya cikin dari.