Rikaken dan ta’addar nan na jihar Zamfara, Bello Turji,ya sako wasu mutane 52 da su ka dade suna garkuwa da su.
Daily Trust ta rawaito cewa, wani dan bindiga da ya yi kaurin suna a jihar Zamfara, Bello Turji, a ranar Litinin din ya sako mutane 52 da su ka dade a hannunsu.
“A halin yanzu a na kwashe wadanda a ka sako daga dajin zuwa wani wuri da a ka amince da su inda za a kai su garin Shinkafi.
“An jera motocin bas kuma an umurce su da su fara tafiya zuwa Maberiya, wani yanki mai tazarar kilomita 5 daga gabashin garin Shinkafi,” wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya.
A watan da ya gabata, Turji ya rubuta wasikar majalisar masarautun Shinkafi, ya na mai jaddada aniyarsa ta ajiye makamansa tare da rungumar zaman lafiya.
Majiyoyi sun ce wani bangare ne na tattaunawa da Turji wanda ya kai ga sako wadanda a ka yi garkuwa da su.