fidelitybank

Tun ina dalibi na ke sayar da Manja da busashen kifi – Kalu

Date:

Tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu ya bayyana irin sana’o’in da ya yi a kasuwanni da dama da kuma yadda ya samu biliyoyin kudade a rayuwar sa.

Kalu, dan majalisar dattawa mai wakiltar yankin Abia ta Arewa kuma bulaliyar majalisar dattawa, mai burin tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Sanatan, a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise a ranar Alhamis, ya ce, ya tsunduma cikin harkokin kasuwanci daban-daban, tun daga sayar da manja zuwa fitar da danyen mai da kuma shigo da sukari daga kasashen waje.

Ya ce, ya kuma kasance ya na yin kwangilar samar da kayan aikin sojojin Najeriya da abinci ga sojoji a fagen fama.

Shahararren marubuci Reuben Abati na cikin ma’aikatan gidan talabijin na Arise da suka yi hira da Sanatan.

Mista Kalu ya ce, ya fara jigilar sayar da manja daga Kudu zuwa Arewa, musamman Maiduguri, tun ya na dalibi a jami’ar Maiduguri.

“Lokacin da na je Maiduguri na gano cewa, Manja na da riba sosai a Maiduguri, ba su da shi. Domin haka duk lokacin da na dawo gida hutu zan sayi Manja in koma. Idan na koma wani hutu, zan sayi busasshen kifi in sayar da su. Haka na fara,” in ji Mista Kalu a cikin hirar.

Sanatan ya ce ya yi karo da Ibrahim Babangida da Muhammadu Buhari ne a lokacin da su ke manyan hafsoshin soji, sai dai bai bayyana yadda mutanen biyu da suka mulki Najeriya suka taimaka masa wajen ci gaban harkokin kasuwancinsa ba.

Ya ce“Ina cikin shigo da sukari da shinkafa da yawa a wani lokaci a rayuwarsa, kuma ya kasance babban abokin takara da Aliko Dangote, mutumin da ya fi kowa kudi a Afirka a yau.

“Na kasance daya daga cikin manyan masu shigo da shinkafa da sukari. A gare ni, samun kudi basira ce. Daga nan na fara gina masana’antu a Aba da Ota.” In ji Kalu.

Ko da ya ke bai yi magana game da wannan ba a cikin hirar Arise TV, Mista Kalu ya na da jari a kafafen yada labarai ya mallaki jaridun Sun da Telegraph.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp