Allah ya yi wa tsohon Ministan Kwadago, Alhaji Hussaini Zanwa Akwanga rasuwa.
Mataimakin shugaban karamar hukumar Akwanga a jihar Nasarawa, Alhaji Safiyanu Isa wanda ya tabbatar da rasuwar tsohon ministan ya ce “tsohon ministan ya rasu ne a yau Juma’a, a Akwanga”
Alhaji Akwanga, ya na da shekaru 77 a duniya bayan ya sha fama da jinya a yankin sa na Akwanga da ke karamar hukumar Akwanga ta jihar Nasarawa.
Tsohon Ministan, kwararren malami, ya zama minista a shekarar 2003, amma shugaban kasa na wancan lokacin, Olusegun Obasanjo ya kore shi.
A shekarar 2017, an yi garkuwa da tsohon ministan a gonarsa da ke kauyen Kurmin Tagwaye, kusa da Akwanga, amma bayan kwana biyu a ka sake shi bayan ya biya kudin fansa.
Tuni dai a ka yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a garinsu na Akwanga.