Ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Yemi Osibanjo (OSO), ta naɗa tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafizu Abubakar, a matsayin shugaban ƙungiyar da zai jagoranci gangamin yaƙin neman zaɓen 2023.
An dai tabbatar da naɗin nasa ne tare da wasu shugabannin tafiyar, yayin wani taron ƙungiyar da ya gudana a Kano ranar Asabar.
Farfesa Hafizu dai shi ne mataimakin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga shekarar 2015 zuwa 2018.
Taron dai ya samu halartar kungiyoyin magoya bayan mataimakin shugaban ƙasar da suka fito daga sassa daban-daban na Najeriya.
Da yake jawabi yayin taron, Daraktan tsare-tsare na kungiyar, Bashir Suwaid, ya ce, akalla ƙungiyoyin da ke goyon bayan Osinbajo sama da 45 ne suka halarci taron.
Aminiya ta rawaito cewa, taron ya kuma zabi shugabanni daga dukkan shiyyoyin siyasa guda shida na ƙasar nan.
Sauran mukaman jagororin ƙungiyar sun hada da daraktan tsare-tsare da mai ba da shawara a bangaren shari’a da daraktan Kudi da na wayar da kan Jljama’a da na mulki da kuma na yaɗa labarai da dai sauransu.