fidelitybank

Tsohon gwamnan Kano zai jagoranci tawagar yaƙin neman zaɓen Osibanjo

Date:

Ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Yemi Osibanjo (OSO), ta naɗa tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafizu Abubakar, a matsayin shugaban ƙungiyar da zai jagoranci gangamin yaƙin neman zaɓen 2023.

An dai tabbatar da naɗin nasa ne tare da wasu shugabannin tafiyar, yayin wani taron ƙungiyar da ya gudana a Kano ranar Asabar.

Farfesa Hafizu dai shi ne mataimakin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga shekarar 2015 zuwa 2018.

Taron dai ya samu halartar kungiyoyin magoya bayan mataimakin shugaban ƙasar da suka fito daga sassa daban-daban na Najeriya.

Da yake jawabi yayin taron, Daraktan tsare-tsare na kungiyar, Bashir Suwaid, ya ce, akalla ƙungiyoyin da ke goyon bayan Osinbajo sama da 45 ne suka halarci taron.

Aminiya ta rawaito cewa, taron ya kuma zabi shugabanni daga dukkan shiyyoyin siyasa guda shida na ƙasar nan.

Sauran mukaman jagororin ƙungiyar sun hada da daraktan tsare-tsare da mai ba da shawara a bangaren shari’a da daraktan Kudi da na wayar da kan Jljama’a da na mulki da kuma na yaɗa labarai da dai sauransu.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp