Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci a Najeriya ta shigar da karar sugaban kasa Muahhamdu Buhari a gaban kotu, bisa zargin da ake yi na batan kudaden da suka kai Naira biliyan 3 daga ma’aikatar kuɗi ta kasa.
Karar ta biyo bayan batan dabon da ake zargin ofishin babban akanta janar na kasa ya shigar a 2018 da 2019 na rahoton da yake fitarwa, wanda aka batar da su ba bisa ka’ida ba ko kuma ba a bayar da bayanansu ba.
Karar mai lamba FHC/L/CS/148/22 an shigar da ita ne a ranar Juma’ar da ta gabata a wata babbar kotun Tarayya da ke Legas, kamar yadda SERAP ta bukata.
SERAP ta ce, umarnin zai sanya Buhari ya tabbatar da an gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan Naira biliyan 3.1, wadanda kudaden mutanen Najeriya ne, a gabatar da duk wanda ake zargi a gaban kotu, kuma a kwato kudaden al’umma. A cewar BBC.