Dan wasan tsakiyar Najeriya, Ubong Moses Ekpai ya koma kulob din Jamhuriyar Czech, FK Milada Boleslav a matsayin aro na tsawon kakar wasa.
Ekpai ya koma Milada Boleslav daga zakaran Jamhuriyar Czech, Slavia Prague.
Tuni dai dan wasan mai shekaru 26 ya fara atisaye tare da sabbin abokan wasansa.
“Mun yi amfani da damar da muka amince a kan aro tare da dan wasan da kuma kulob din, shi ne mai sauri irin na kwallon kafa wanda ya san yadda za a kewaya a bugun fanareti na abokin hamayyar,” kocin Mlada Boleslav, Pavel Hoftych ya shaida wa shafin yanar gizon kulob din.
“Lokacin da ya kama jin dadin kungiyar, dan wasa ne da ke da bambanci, tare da zuwansa mun ninka zabin mu a kan fuka-fuki.”
Ekpai ya buga wasa a kungiyoyin kwallon kafa na Najeriya, Akwa United da Kano Pillars kafin ya koma kasar Isra’ila a shekarar 2019.