fidelitybank

Tsoffin ɗaliban BUK sun bada N500,000 tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi

Date:

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero Kano, BUK, aji na shekarar 1989, sun baiwa jami’ar naira dubu 500 domin tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi ƴan asalin Jihar Kano.

Shugaban ƙungiyar, Dakta Kabiru Jinjiri Ringim ne ya baiyana hakan yayin da ya jagoranci wasu mambobin ƙungiyar zuwa ziyara ga Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ofishin sa a jiya Juma’a.

Dakta Jinjiri ya ce “ƙungiyar ta tanadi tsare-tsare duk shekara a ƙoƙarin ta na tallafawa marasa ƙarfi, musamman a ɓangaren ilimi,”

A jawabin shi, Shugaban na BUK, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar bisa wannan abin alheri da ta yi.

Ya ƙara da cewa a ƙoƙarin ta na tallafawa ɗalibai ƴan jihar, jami’ar ta ɓullo da wani tsari na ɗaukar aiki, inda jami’ar ta ɗauki ɗalibai 125 aiki na wucin-gadi a karon farko.

Shugaban makarantar, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa na ɓangaren aiyukan gudanarwa, Farfesa Mahmud Umar Sani ya ce tsarin wani yunƙuri ne na tallafawa ɗalibai da kuma rage musu raɗaɗin fatara.

Ya kuma ƙara da cewa tallafin da kungiyar tsoffin ɗaliban ta bayar ya zo a daidai lokacin da a ke buƙatarsa.

 

 

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp