fidelitybank

Tsoffin ɗaliban BUK sun bada N500,000 tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi

Date:

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero Kano, BUK, aji na shekarar 1989, sun baiwa jami’ar naira dubu 500 domin tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi ƴan asalin Jihar Kano.

Shugaban ƙungiyar, Dakta Kabiru Jinjiri Ringim ne ya baiyana hakan yayin da ya jagoranci wasu mambobin ƙungiyar zuwa ziyara ga Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ofishin sa a jiya Juma’a.

Dakta Jinjiri ya ce “ƙungiyar ta tanadi tsare-tsare duk shekara a ƙoƙarin ta na tallafawa marasa ƙarfi, musamman a ɓangaren ilimi,”

A jawabin shi, Shugaban na BUK, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar bisa wannan abin alheri da ta yi.

Ya ƙara da cewa a ƙoƙarin ta na tallafawa ɗalibai ƴan jihar, jami’ar ta ɓullo da wani tsari na ɗaukar aiki, inda jami’ar ta ɗauki ɗalibai 125 aiki na wucin-gadi a karon farko.

Shugaban makarantar, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa na ɓangaren aiyukan gudanarwa, Farfesa Mahmud Umar Sani ya ce tsarin wani yunƙuri ne na tallafawa ɗalibai da kuma rage musu raɗaɗin fatara.

Ya kuma ƙara da cewa tallafin da kungiyar tsoffin ɗaliban ta bayar ya zo a daidai lokacin da a ke buƙatarsa.

 

 

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...
X whatsapp