fidelitybank

Tsoffin ɗaliban BUK sun bada N500,000 tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi

Date:

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero Kano, BUK, aji na shekarar 1989, sun baiwa jami’ar naira dubu 500 domin tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi ƴan asalin Jihar Kano.

Shugaban ƙungiyar, Dakta Kabiru Jinjiri Ringim ne ya baiyana hakan yayin da ya jagoranci wasu mambobin ƙungiyar zuwa ziyara ga Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ofishin sa a jiya Juma’a.

Dakta Jinjiri ya ce “ƙungiyar ta tanadi tsare-tsare duk shekara a ƙoƙarin ta na tallafawa marasa ƙarfi, musamman a ɓangaren ilimi,”

A jawabin shi, Shugaban na BUK, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar bisa wannan abin alheri da ta yi.

Ya ƙara da cewa a ƙoƙarin ta na tallafawa ɗalibai ƴan jihar, jami’ar ta ɓullo da wani tsari na ɗaukar aiki, inda jami’ar ta ɗauki ɗalibai 125 aiki na wucin-gadi a karon farko.

Shugaban makarantar, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa na ɓangaren aiyukan gudanarwa, Farfesa Mahmud Umar Sani ya ce tsarin wani yunƙuri ne na tallafawa ɗalibai da kuma rage musu raɗaɗin fatara.

Ya kuma ƙara da cewa tallafin da kungiyar tsoffin ɗaliban ta bayar ya zo a daidai lokacin da a ke buƙatarsa.

 

 

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp