fidelitybank

Tsoffin Ɗaliban BUK ƴan shekarar 1992 sun bada tallafin naira miliyan 1 ga ɗalibai

Date:

 

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero ta Kano, BUK, ƴan shekarar 1992 sun ci alwashin ɗorewa da bada tallafin naira miliyan 1 a kowacce shekara ga ɗalibai ƴan asalin Jihar Kano.

Ƙungiyar ta fara bada wannan tallafi ne sama da shekaru biyar da su ka gabata.

Bayan tallafin karatun, ƙungiyar kuma na bada wasu taimakon ga ɗalibai da ma jami’ar baki ɗaya a duk lokacin da ta ke yin taron sada zumunci a duk shekara.

Shugaban ƙungiyar, Ɗahiru Sa’id, yayin da ya ke jawabi a taron sada zumunci na bana, karo na 6 kenan, ya ce tallafin karatun wani ɓangare ne na taimakon da su ke bayarwa.

Ya ce “ƙungiyar ta samu nasarori da dama, da su ka haɗa da tallafin karatu na Naira miliyan 1 duk shekara ga ɗalibai ƴan asalin jihar Kano, marasa ƙarfi domin su samu damar biyan kuɗin makaranta.

“Haka kuma mu na tallafawa iyalan waɗanda su ka rasu a cikin mu. Mu na kuma fitar da ɗaurararru da ga gidajen yari da kuma kai ziyara zuwa gidajen marayu.

“mun kuma tallafawa waɗanda su ka samu ibtila’in ambaliyar ruwa, sannan mu na taimakawa marasa lafiya ƴan jihar Kano a asibitoci a faɗin jihar. Sannan kuma muna tallafawa junan mu idan ɗayan mu zai yi aure ko suna da sauran bukukuwa,” in ji Sa’id.

Ya kuma ƙara da cewa tun sanda a ka kafa ƙungiyar a 2016, ba ta taɓa gajiyawa wajen taimakon da yanke bayarwa ba, duk da halin da tattalin arziƙi ya faɗa sakamakon annobar korona.

Tun da fari dai ƙungiyar, a bisa jagorancin Farfesa Hajara Sanda, ta miƙa cekin naira miliyan 1 ga Shuagaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ranar Juma’a.

Da ya ke jawabi bayan karɓar cekin kuɗin, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar, in da kuma yi kira ga sauran ƙungiyoyin tsoffin ɗalibai da su kwaikwayi irin aiyukan alherin da ƴan shekarar 1992 ɗin ke yi.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp