fidelitybank

Tsoffin Ɗaliban BUK ƴan shekarar 1992 sun bada tallafin naira miliyan 1 ga ɗalibai

Date:

 

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero ta Kano, BUK, ƴan shekarar 1992 sun ci alwashin ɗorewa da bada tallafin naira miliyan 1 a kowacce shekara ga ɗalibai ƴan asalin Jihar Kano.

Ƙungiyar ta fara bada wannan tallafi ne sama da shekaru biyar da su ka gabata.

Bayan tallafin karatun, ƙungiyar kuma na bada wasu taimakon ga ɗalibai da ma jami’ar baki ɗaya a duk lokacin da ta ke yin taron sada zumunci a duk shekara.

Shugaban ƙungiyar, Ɗahiru Sa’id, yayin da ya ke jawabi a taron sada zumunci na bana, karo na 6 kenan, ya ce tallafin karatun wani ɓangare ne na taimakon da su ke bayarwa.

Ya ce “ƙungiyar ta samu nasarori da dama, da su ka haɗa da tallafin karatu na Naira miliyan 1 duk shekara ga ɗalibai ƴan asalin jihar Kano, marasa ƙarfi domin su samu damar biyan kuɗin makaranta.

“Haka kuma mu na tallafawa iyalan waɗanda su ka rasu a cikin mu. Mu na kuma fitar da ɗaurararru da ga gidajen yari da kuma kai ziyara zuwa gidajen marayu.

“mun kuma tallafawa waɗanda su ka samu ibtila’in ambaliyar ruwa, sannan mu na taimakawa marasa lafiya ƴan jihar Kano a asibitoci a faɗin jihar. Sannan kuma muna tallafawa junan mu idan ɗayan mu zai yi aure ko suna da sauran bukukuwa,” in ji Sa’id.

Ya kuma ƙara da cewa tun sanda a ka kafa ƙungiyar a 2016, ba ta taɓa gajiyawa wajen taimakon da yanke bayarwa ba, duk da halin da tattalin arziƙi ya faɗa sakamakon annobar korona.

Tun da fari dai ƙungiyar, a bisa jagorancin Farfesa Hajara Sanda, ta miƙa cekin naira miliyan 1 ga Shuagaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ranar Juma’a.

Da ya ke jawabi bayan karɓar cekin kuɗin, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar, in da kuma yi kira ga sauran ƙungiyoyin tsoffin ɗalibai da su kwaikwayi irin aiyukan alherin da ƴan shekarar 1992 ɗin ke yi.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp