fidelitybank

Tsoffin ɗaliban BUK sun bada N500,000 tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi

Date:

 

Ƙungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Bayero Kano, BUK, aji na shekarar 1989, sun baiwa jami’ar naira dubu 500 domin tallafin karatu ga ɗalibai marasa ƙarfi ƴan asalin Jihar Kano.

Shugaban ƙungiyar, Dakta Kabiru Jinjiri Ringim ne ya baiyana hakan yayin da ya jagoranci wasu mambobin ƙungiyar zuwa ziyara ga Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas a ofishin sa a jiya Juma’a.

Dakta Jinjiri ya ce “ƙungiyar ta tanadi tsare-tsare duk shekara a ƙoƙarin ta na tallafawa marasa ƙarfi, musamman a ɓangaren ilimi,”

A jawabin shi, Shugaban na BUK, Farfesa Abbas ya yabawa ƙungiyar bisa wannan abin alheri da ta yi.

Ya ƙara da cewa a ƙoƙarin ta na tallafawa ɗalibai ƴan jihar, jami’ar ta ɓullo da wani tsari na ɗaukar aiki, inda jami’ar ta ɗauki ɗalibai 125 aiki na wucin-gadi a karon farko.

Shugaban makarantar, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa na ɓangaren aiyukan gudanarwa, Farfesa Mahmud Umar Sani ya ce tsarin wani yunƙuri ne na tallafawa ɗalibai da kuma rage musu raɗaɗin fatara.

Ya kuma ƙara da cewa tallafin da kungiyar tsoffin ɗaliban ta bayar ya zo a daidai lokacin da a ke buƙatarsa.

 

 

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp