Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi kira ga tsofaffin daliban makarantu cewa da su mayar da hankali wajen taimakawa makarantun da su ka kammala a lokacin da su ka zama wasu.
Sarkin ya bayyana haken ne ya yin da tsofaffin daliban makarantar Firamaner ta Kofar Kudu su ka kawo masa ziyara a fadarsa.
Aminu Ado Bayero ya ce,”Za mu ci gaba da baiwa dalibai gudunmuwa wajen ganin an taimakawa ilimi a jihar Kano dama kasa baki daya, kuma ya kamata duk wanda ya tsinci kansa a wani hali na ci gaba ya taimakawa makarantar da ya kammala”.
A nasa jawabin shugaban kungiyar tsofaffin daliban makarantar, Kofar Kudu, Abubakar Shehu Kwaru ya ce sun kawo ziyara ne ga Sarkin da kuma ta yi shi murna.