Wasu gungun ‘yan bindiga sun rubuta wasika ga mabiya addinin Kirista a jihar Zamfara da ke Arewa Maso yammacin Najeriya cewa da su rufe coci-coci ko kuma su fuskanci munanan hare-hare.
A tattaunawa da Saharareporters, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Shehu, ya ce ‘yan sanda sun san da wasikar barazanar, kuma suna kan gaba wajen shawo lamarin.
Ya ce, “Eh, zan iya tabbatar da cewa gaskiya ne, an aike da wasikar barazanar ga Kiristocin Jihar Zamfara su daina ibada da kuma rufe Coci. A gaskiya ‘yan sanda sun sanar da shugabannin addinin Kirista game da barazanar. Haka zalika kwamishina ‘yan sanda ya gayyaci shugabannin kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN a jihar, domin tattauna matakan tsaro a kan lamarin, dangane da haka, kwamishinan ya samar da wata tawaga ta musamman da za ta rika sintiri tare da kare masu ibada, musamman a ranar Lahadi. Bugu da ƙari, an tura ma’aikatan sanye da kayan aiki, domin tattara bayanan sirri da kuma bankado waɗanda ke da hannu a cikin wasikar barazanar,” in ji shi.
A ranar Lahadin da ta gabata ne wani daga cikin shugaban addinin Kirista da ya nemi a sakaya sunansa ya bukaci mabiya addinin Kirista a sassan duniya da su yi addu’a kan halin da suke ciki a Zamfara da sauran sassan Arewacin Najeriya.