fidelitybank

Tsaro: ‘Yan ta’adda sun aike da wasika ga mabioya addinin Kirista a Zamfara

Date:

Wasu gungun ‘yan bindiga sun rubuta wasika ga mabiya addinin Kirista a jihar Zamfara da ke Arewa Maso yammacin Najeriya cewa da su rufe coci-coci ko kuma su fuskanci munanan hare-hare.

A tattaunawa da Saharareporters, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Shehu, ya ce ‘yan sanda sun san da wasikar barazanar, kuma suna kan gaba wajen shawo lamarin.

Ya ce, “Eh, zan iya tabbatar da cewa gaskiya ne, an aike da wasikar barazanar ga Kiristocin Jihar Zamfara su daina ibada da kuma rufe Coci. A gaskiya ‘yan sanda sun sanar da shugabannin addinin Kirista game da barazanar. Haka zalika kwamishina ‘yan sanda ya gayyaci shugabannin kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN a jihar, domin tattauna matakan tsaro a kan lamarin, dangane da haka, kwamishinan ya samar da wata tawaga ta musamman da za ta rika sintiri tare da kare masu ibada, musamman a ranar Lahadi. Bugu da ƙari, an tura ma’aikatan sanye da kayan aiki, domin tattara bayanan sirri da kuma bankado waɗanda ke da hannu a cikin wasikar barazanar,” in ji shi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne wani daga cikin shugaban addinin Kirista da ya nemi a sakaya sunansa ya bukaci mabiya addinin Kirista a sassan duniya da su yi addu’a kan halin da suke ciki a Zamfara da sauran sassan Arewacin Najeriya.

 

 

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp