fidelitybank

Tsaro: ‘Yan ta’adda sun aike da wasika ga mabioya addinin Kirista a Zamfara

Date:

Wasu gungun ‘yan bindiga sun rubuta wasika ga mabiya addinin Kirista a jihar Zamfara da ke Arewa Maso yammacin Najeriya cewa da su rufe coci-coci ko kuma su fuskanci munanan hare-hare.

A tattaunawa da Saharareporters, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Shehu, ya ce ‘yan sanda sun san da wasikar barazanar, kuma suna kan gaba wajen shawo lamarin.

Ya ce, “Eh, zan iya tabbatar da cewa gaskiya ne, an aike da wasikar barazanar ga Kiristocin Jihar Zamfara su daina ibada da kuma rufe Coci. A gaskiya ‘yan sanda sun sanar da shugabannin addinin Kirista game da barazanar. Haka zalika kwamishina ‘yan sanda ya gayyaci shugabannin kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN a jihar, domin tattauna matakan tsaro a kan lamarin, dangane da haka, kwamishinan ya samar da wata tawaga ta musamman da za ta rika sintiri tare da kare masu ibada, musamman a ranar Lahadi. Bugu da ƙari, an tura ma’aikatan sanye da kayan aiki, domin tattara bayanan sirri da kuma bankado waɗanda ke da hannu a cikin wasikar barazanar,” in ji shi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne wani daga cikin shugaban addinin Kirista da ya nemi a sakaya sunansa ya bukaci mabiya addinin Kirista a sassan duniya da su yi addu’a kan halin da suke ciki a Zamfara da sauran sassan Arewacin Najeriya.

 

 

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp