Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Najeriya (CDS), Janar Leo Irabor, ya umarci Janar-Janar 50 na rundunar sojin Najeriya da su mika takardar murabus dinsu nan take.
Kamar yadda shafin jaridar Daily Post ya rawaito cewa, jami’an sun hadar da na rundunar sojojin saman Najeriya, sojojin kasa da kuma na ruwa; kusan 25 daga cikin manyan hafsoshi na cikin rundunar.
Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa Irabor ya bayar da umarnin ne a shelkwatar tsaro da ke Abuja ranar Litinin.
A taron da a ka yi da karfe 2:00 na rana, Irabor ya yi musu godiya bisa hidimar da su ka yi, kuma ya shaida wa duk wadanda suka halarci taron cewa lokaci ya yi da za su bar ofis.
Amma akwai wasu Course Janar 36 har yanzu suna da fiye da shekaru uku kafin su yi ritaya.
“Su kusan 50; biyu daga cikinsu a sojojin, za su yi ritaya a shekarar 2022, yayin da sauran kusan shekaru uku da rabi ne ya rage musu su kammala aiki,” inji majiyar.