fidelitybank

Tsaro: Mafarauta sun shirya sadaukar da kansu domin yaki da ‘yan ta’adda

Date:

Kungiyar mafarauta ta Najeriya, ta yi alkawarin tallafa wa hukumomin tsaro, domin yaki da garkuwa da mutane, da fashi da makami, da sauran matsalolin rashin tsaro da kasar nan ke fuskanta a halin yanzu.

Shugaban kungiyar na kasa, Muhammadu Usman Baba Tola ya bayyana hakan a Bauchi a wajen taron shekara-shekara da kaddamar da sabbin jami’an kungiyar da a ka gudanar a dandalin Ibrahim Badamasi Babangida da ke Bauchi.

Ya ce, za a samu gagarumar nasara idan mafarauta da jami’an tsaro suka hada kai, domin cimma wata manufa guda.

Ya ce tabbatar da zaman lafiya a Najeriya shi ne babban abin da kowane mafarauci ke da shi a kasar, domin haka ya yi alkawarin cewa mafarauta a shirye suke su tunkari ‘yan bindiga da masu tayar da kayar baya a maboyarsu.

“Mafarauta sun san dazuzzuka da tsaunuka na Najeriya, za su iya taimakawa sosai ta wannan hanyar, mun hadu a Bauchi daga sassan Najeriya a yau domin sake duba al’amuran da su ka shafi kasa tare da sanin yadda za mu iya shigo da mu don taimakawa wajen magance wadannan matsalolin. mafi kyawun kasarmu,” inji Tola.

Ya bayyana cewa tuntubar gwamnati da sarakunan gargajiya da hukumomin tsaro na daga cikin hanyoyin da su ke bi.

Ya kuma jaddada cewa a shirye su ke su taimakawa masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a kasar da nufin shawo kan matsalar rashin tsaro.

A nasa jawabin gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya yi alkawarin tallafawa mafarauta da gwamnatinsa za ta ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, domin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar baki daya.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin babban sakataren sa Sama’ila Burga, ya yaba da gudunmawar da mafarauta ke bayarwa wajen tabbatar da tsaro a jihar Bauchi tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro na gwamnati.

 

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp