Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya ce jiran tsammanin da al’umma ke yi wa shugaba Muhammadu Buhari, sama da wanda ya ke yi a yanzu, daidai ya ke da jiran gawon shanu.
Obasanjo ya bayyana hakan ne ranar Litinin, yayin wani taro kan hanyoyin bunkasa tsaro da wata kungiya ta Global Peace Foundation and Vision Africa ta shirya a Abuja.
Ya ce, “Gaskiya daya ce, Buhari ya yi iya bakin kokarinsa, Idan mu ka ce sai ya yi sama da haka, to tabbas yaudarar kan mu mu ke yi. Ina mu ka dosa kenan? Ba zai yi wu mu zauna mu nade hannuwan mu ba kawai, na yi amanna wannan na daga cikin abubuwan da muke yi. Kuma ta yaya Najeriya za ta kasance bayan ya tafi? Addu’a ta ita ce Allah Ya ba shi tsawon rai ya kammala mulkin nan lafiya”.
Ya ci gaba da cewa, “Amma mai ya kamata mu yi wajen inganta yanayin da mu ke ciki a yanzu? Wannan nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa baki daya”. A cewar Obasanjo.
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya kuma ce, amfani da karfin soja kadai ba zai kawo karshen matsalar ta’addanci ba a Najeriya, dole sai an hada da wasu dabarun domin a tsira tare.