Kungiyar Yoruba ta Afenifere, ta yi kira ga shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a cikin gaggawa, ya nemi taimakon kasashen waje saboda karuwar matsalolin rashin tsaro a kasar wanda ya bijirewa duk wani nau’in mafita na cikin gida.
Kungiyar Yarbawa a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ta kuma yi kira ga shugaban kasar da ya duba yiwuwar sake kiran jami’an leken asirin da su ka yi ritaya, domin yabawa kokarin jami’an tsaron da a ke da su na dakatar da abin da ta bayyana a matsayin yaki a kasar.
Sanarwar mai dauke da sa hannun Sakataren yada labarai na kungiyar ta Afenifere, Jare Ajayi, ta bayyana cewa, matsalar rashin tsaro a kasar nan ya wuce maganganu kawai, domin babu sauran lokacin batawa.
Kungiyar ta kara da cewa lokaci ya yi da ya kamata Buhari ya kasance mai gaskiya da yanke hukunci da kuma dukufa wajen tunkarar matsalar tsaro, domin hana al’ummar kasar shiga cikin mawuyacin hali.