fidelitybank

Tsaro: Ba ma iya barci da ido biyu ni da gwamna na – Sarkin Katsina

Date:

Mai martaba sarkin Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman, ya shaida wa mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, cewa da shi da gwamnan, Aminu Bello Masari, sam ba sa iya barci da ido biyu, saboda kalubalen tsaron da ya addabi jihar.

Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi ga mataimakin shugaban kasar, wanda ya kai masa ziyarar ta’aziyya, saboda rasuwar mahaifiyar attajirin nan, Alhaji Dahiru Mangal ranar Lahadi.

A cewarsa, “Wannan zuwan naka a karon farko tun da ka fara yakin neman zabe zuwa ne mai cike da tarihi a wajenmu. Yanzu a gida kake, kuma ka yi magana a kan matsalar tsaro, wadda ita ce babbar matsalar da ta dame mu. Ban jima da dawowa daga Kaduna ba, inda ina zuwa na iske kusan kiran waya 100 a kan wani shiri da ’yan ta’adda ke yi na kai hari, wanda a yanzu ya zama ruwan dare.

“Ni da Gwamna Masari, ba mu da wani lokacin da muke iya yin barci da idanunmu biyu a rufe, amma na yi matukar farin ciki da aka ayyana wadannan miyagun a matsayin ’yan ta’adda,” inji Sarkin.

Tun da farko dai a nasa jawabin, Farfesa Osinbajo ya ce, ya yi matukar murna da ya ji an ce yanayin tsaron jihar na dada inganta, kamar yadda Masari ya shaida masa.

“Shugaban Kasa ya tattauna da dukkan kwararru a sha’anin tsaro, kuma za a yi canji a inda ya kamata, domin a samu ingantuwar tsaro a fadin kasa”. A cewar Osibanjo kamar yadda Aminiya ta rawaito.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp