fidelitybank

Tsaro: Ba ma iya barci da ido biyu ni da gwamna na – Sarkin Katsina

Date:

Mai martaba sarkin Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman, ya shaida wa mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, cewa da shi da gwamnan, Aminu Bello Masari, sam ba sa iya barci da ido biyu, saboda kalubalen tsaron da ya addabi jihar.

Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi ga mataimakin shugaban kasar, wanda ya kai masa ziyarar ta’aziyya, saboda rasuwar mahaifiyar attajirin nan, Alhaji Dahiru Mangal ranar Lahadi.

A cewarsa, “Wannan zuwan naka a karon farko tun da ka fara yakin neman zabe zuwa ne mai cike da tarihi a wajenmu. Yanzu a gida kake, kuma ka yi magana a kan matsalar tsaro, wadda ita ce babbar matsalar da ta dame mu. Ban jima da dawowa daga Kaduna ba, inda ina zuwa na iske kusan kiran waya 100 a kan wani shiri da ’yan ta’adda ke yi na kai hari, wanda a yanzu ya zama ruwan dare.

“Ni da Gwamna Masari, ba mu da wani lokacin da muke iya yin barci da idanunmu biyu a rufe, amma na yi matukar farin ciki da aka ayyana wadannan miyagun a matsayin ’yan ta’adda,” inji Sarkin.

Tun da farko dai a nasa jawabin, Farfesa Osinbajo ya ce, ya yi matukar murna da ya ji an ce yanayin tsaron jihar na dada inganta, kamar yadda Masari ya shaida masa.

“Shugaban Kasa ya tattauna da dukkan kwararru a sha’anin tsaro, kuma za a yi canji a inda ya kamata, domin a samu ingantuwar tsaro a fadin kasa”. A cewar Osibanjo kamar yadda Aminiya ta rawaito.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp