fidelitybank

Tsaro: Amurka da Rasha za su gana a kan Ukraine

Date:

Jami’an Amurka da na Rasha za su yi shawarwari kan harkokin tsaro a ranar 10 ga watan Janairu domin tattauna damuwarsu game da ayyukan sojan da su ke yi da kuma tunkarar tashin hankalin da a ke yi kan kasar Ukraine.

Mai magana da yawun gwamnatin Biden ne ya sanar da ranar da yammacin jiya Litinin, kuma ya ce akwai yiwuwar Rasha da NATO suma za su yi tattaunawa a ranar 12 ga watan Janairu, inda za a yi wani babban taro da suka hada da Moscow, Washington da sauran kasashen Turai a ranar 13 ga watan Janairu.

Mataimakin ministan harkokin wajen Rasha Sergei Ryabkov ya tabbatar da wadannan ranakun a jiya Talata, ya kuma ce yana fatan tattaunawar da Amurka za ta yi a Geneva za ta kaddamar da wani tsari da zai bai wa Moscow wani sabon garantin tsaro daga kasashen yammacin duniya.

Wannana matakin dai wani dogon buri ne na Moscow, wanda ya firgita kasashen Yamma ta hanyar tara dubunnan dakaru kusa da Ukraine cikin watanni biyun da suka gabata.

Ryabkov ya ce, za a gudanar da taron kungiyar tsaro ta NATO a ranar 12 ga watan Janairu a Brussels na kasar Belgium, yayin da tattaunawar ta ranar 13 ga wata za ta kunshi kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai mai shelwata a Vienna, wadda ta hada da Amurka da kawayenta na NATO, da kuma Rasha da Ukraine da sauran tsoffin jihohin Soviet.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke É—auka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da Æ™arfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naÉ—a kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka Æ´anbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe Æ´anbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp