fidelitybank

Tsaro: Amurka da Rasha za su gana a kan Ukraine

Date:

Jami’an Amurka da na Rasha za su yi shawarwari kan harkokin tsaro a ranar 10 ga watan Janairu domin tattauna damuwarsu game da ayyukan sojan da su ke yi da kuma tunkarar tashin hankalin da a ke yi kan kasar Ukraine.

Mai magana da yawun gwamnatin Biden ne ya sanar da ranar da yammacin jiya Litinin, kuma ya ce akwai yiwuwar Rasha da NATO suma za su yi tattaunawa a ranar 12 ga watan Janairu, inda za a yi wani babban taro da suka hada da Moscow, Washington da sauran kasashen Turai a ranar 13 ga watan Janairu.

Mataimakin ministan harkokin wajen Rasha Sergei Ryabkov ya tabbatar da wadannan ranakun a jiya Talata, ya kuma ce yana fatan tattaunawar da Amurka za ta yi a Geneva za ta kaddamar da wani tsari da zai bai wa Moscow wani sabon garantin tsaro daga kasashen yammacin duniya.

Wannana matakin dai wani dogon buri ne na Moscow, wanda ya firgita kasashen Yamma ta hanyar tara dubunnan dakaru kusa da Ukraine cikin watanni biyun da suka gabata.

Ryabkov ya ce, za a gudanar da taron kungiyar tsaro ta NATO a ranar 12 ga watan Janairu a Brussels na kasar Belgium, yayin da tattaunawar ta ranar 13 ga wata za ta kunshi kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai mai shelwata a Vienna, wadda ta hada da Amurka da kawayenta na NATO, da kuma Rasha da Ukraine da sauran tsoffin jihohin Soviet.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp