fidelitybank

Tinubu ya fara sulhu tsakanin Ganduje da Shekarau

Date:

 

 

Yayin da rikicin jam’iya mai mulki, APC ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a Jihar Kano, a na ta samun yunƙurin sasanta ɓangarorin da ke zaman doya da manja a jihar.

Bayan da kwamitin sulhu da APC ta kafa ya fara aiki a makon da ya gabata, inda ya yi iƙrarin cewa ya sulhunta tsakanin Gwamna mai ci, Abdullahi Ganduje da tsohon gwamna, Ibrahim Shekarau, alamu dai sun nuna cewa har yanzu a kwai sauran rina a kaba a game da dambarwar siyasar da ta dabaibaye jam’iyar a jihar.

Sai dai kuma, rahotanni sun nuna cewa, Jagoran APC na ƙasa, Bola Tinubu ya fara na shi yunƙurin na sasanta ɓangarori biyun a jam’iyar a Kano.

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa a jiya Lahadi, Tinubu, wanda shine tsohon gwamnan Jihar Legas, ya gaiyaci Shekarau kuma sun haɗu a Legas ɗin domin sulhu tsakanin sa da abokin burmin sa, Ganduje.

Haka-zalika jaridar ta jiyo cewa shi ma Gandujen, Tinubu ya gaiyace shi, to amma ba ya ƙasar kuma da zarar ya dawo, to zai je Legas ɗin domin su tattauna da jagoran APC ɗin don shawo kan lamarin.

Tuni dai APC ta dare gida biyu a Kano, inda ɓangaren Ganduje da tsagin Shekarau ke iƙirarin cewa shine mai riƙe da shugabacin jam’iya.

A kwanannan ne dai wata babbar kotu a Abuja ta rushe shugabacin jam’iyar na jiha, ƙarƙashin Abdullahi Abbas na tsagin Ganduje, ta kuma tabbatar da Ahmadu Ɗanzago na ɓangaren Shekarau a matsayin shugaban APC a Kano.

 

 

 

 

 

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp