fidelitybank

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Date:

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan Yulin shekarar 2025 a matsayin hutu domin jimamin rasuwar tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin cikin gida na ƙasar ta fitar, wanda babban sakataren ma’aikatar Magdalene Ajani ta sanya wa hannu, inda ta ce wannan ɗoriya ce kan sanar da kwana bakwai na jimamin rasuwar.

Ministan Harkokin Cikin Gidan ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya yi sanarwar a madadin shugaban ƙasar, Bola Tinubu.

Ministan ya ce ƙasar ta ayyana hutun ne domin nuna irin girmamawar da gwamnatin ke yi wa tsohon shugaban, da kuma godiya ga hidima da sadauwar da ya yi domin ciyar da ƙasar gaba.

“Muhammadu Buhari ya mulki Najeriya da gaskiya da amana da kuma matuƙar sadaukarwa musamman wajen haɗin kan Najeriya da cigabanta. Wannan hutun dama ne ga ƴan Najeriya domin tuna irin sadaukarwar da Buhari ya yi.”

Ya yi kira ga ƴan Najeriya su tuna mamacin ta hanyar koyi da shi wajen ɗabbaƙa zaman lafiya da son cigaban ƙasar da aka san marigayin da su.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp