Godswill Akpabio ya bayyana cewa. jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu, za su yi nasara a 2023.
Tsohon gwamnan Akwa Ibom ya lura cewa jam’iyyar APC da Tinubu na da cancanta, iya aiki, da kuma karbuwar da ake bukata.
Akpabio, tsohon ministan Neja Delta, shi ne dan takarar jam’iyyar APC a mazabar Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma.
Ya yi wannan jawabi ne a garin Ukana ranar Lahadi a wajen taron ‘yan jam’iyyar da magoya bayan shiyyar Sanata.
“Ku fita kuje ku yi wa dukkan ‘yan takararmu yakin neman zabe domin jam’iyyar tana da duk abin da ya kamata don lashe zabe daga kasa zuwa jihohi,” Akpabio ya shaida musu.
Dan siyasar ya bayyana Tinubu a matsayin mai rike da tuta mai dimbin tarihi da gudanar da mulki na gari da kuma gudanar da mulkin Najeriya.
Akpabio ya kira tsohon shugaban na Legas “gwabataccen shugaba kuma amintacce” wanda ke shiga gasar a matsayin wanda ya samu nasara.
“Tsarin shugaban kasa na wani ne da zai iya bayarwa kuma Asiwaju Tinubu ya wakilci hakan,” NAN ta ruwaito yana cewa.
Akpabio ya yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan sakin fasinjojin jirgin da aka yi garkuwa da su da kuma gadar Neja ta biyu da za a kaddamar a watan Disamba.