fidelitybank

Teloli da masu sayar da kaya ku kiyaye sanya mutum-mutumi – Hisba

Date:

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce, har yanzu haramcin da ta sanya kan amfani da mutum-mutumi a shagunan sayar da kayan sa wa da na teloli a fadin Jihar na nan daram.

A watan Yunin bara ne dai hukumar ta sanar da haramta amfani da mutum-mutumin a Jihar, tare da barazanar kama duk wanda ya karya dokar.

A cewar Babban Kwamandan hukumar, Harun Ibn Sina, sun dauki matakin ne, saboda amfani da mutum-mutumin ya saba da koyarwar addinin Musulunci.

Sai dai a wani taro da ta yi da Kungiyar Teloli ta Kasa reshen Jihar ranar Alhamis, hukumar ta Hisbah ta sake jaddada cewa, haramcin na nan daram.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen yada labarai na hukumar ya fitar a ranar Juma’a.

A cewar Ibn Sina yayin taron nasa da telolin “Hukumar Hisba ta Jihar Kano bisa dogaro da sashen dokar Hisba ta shekarar 2001, wacce aka yi wa kwaskwarima a 2003, ta hana kowanne mai dinki saka mutum-mutumi, wanda yake dauke da siffar mutum cikakkiya, ko ta mace ko ta namiji.

“Amma za a iya anfani da wanda babu kai ajikinsa ko a jikanta, ita ’yar tsanar da ake saka wa kaya.

“Wannan shine kadan daka cikin muhimman abin da aka tattauna a kai yau,” inji Ibn Sina.

Hukumar Hisbah ta bukaci Teloli da su bi dokar ta hukumar tare da neman su tsaftace sana’ar tasu.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp