fidelitybank

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa birnin Madina na Masarautar Saudiyya domin halartar jana’izar fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijo, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata.

Gwamnan ya tashi daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da daren Litinin, inda ya bayyana girmamawa da mutunta rayuwar marigayin a matsayin wani babban uba ga al’umma.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Abba Yusuf yana tare da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II da gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, da tsohon gwamnan Jigawa, Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sauran manyan jami’an gwamnati da dattawan jihar Kano.

Marigayi Aminu Dantata, wanda ya shahara wajen kasuwanci da sadaka da hidimar jama’a, ya rasu ne a Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa.

“Mutuwarsa ta bar giɓi a harkokin tattalin arziki da walwalar al’umma, tare da kammala wani babi mai muhimmanci a tarihin Najeriya.” in ji sanarwar.

Gwamnan yayin da yake zantawa da manema labarai kafin tafiyar, ya bayyana cewa marigayin yana da kyakkyawan tarihi na karamci da kishin jama’a wanda ya zarce ƙasashe da iyakoki.

“Halartar tawagar Kano a jana’izar alama ce ta matuƙar girmamawa da godiyar da al’ummar Kano ke da ita ga irin gudummawar da marigayin ya bayar a rayuwarsa.” sanarwar ta ƙara da cewa

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...
X whatsapp