Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa birnin Madina na Masarautar Saudiyya domin halartar jana’izar fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijo, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata.
Gwamnan ya tashi daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da daren Litinin, inda ya bayyana girmamawa da mutunta rayuwar marigayin a matsayin wani babban uba ga al’umma.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Abba Yusuf yana tare da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II da gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, da tsohon gwamnan Jigawa, Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sauran manyan jami’an gwamnati da dattawan jihar Kano.
Marigayi Aminu Dantata, wanda ya shahara wajen kasuwanci da sadaka da hidimar jama’a, ya rasu ne a Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa.
“Mutuwarsa ta bar giɓi a harkokin tattalin arziki da walwalar al’umma, tare da kammala wani babi mai muhimmanci a tarihin Najeriya.” in ji sanarwar.
Gwamnan yayin da yake zantawa da manema labarai kafin tafiyar, ya bayyana cewa marigayin yana da kyakkyawan tarihi na karamci da kishin jama’a wanda ya zarce ƙasashe da iyakoki.
“Halartar tawagar Kano a jana’izar alama ce ta matuƙar girmamawa da godiyar da al’ummar Kano ke da ita ga irin gudummawar da marigayin ya bayar a rayuwarsa.” sanarwar ta ƙara da cewa