Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026.
Bankin ya bayyana haka ne a rahotonsa na hasashen tattalin arzikin duniya na 2025 da ya fitar a ranar Alhamis, 17 ga watan Janairu mai taken Global Economic Prospects January 2025.
“Tattalin arzikin yankin hamadar Afirka zai haɓaka da kashi 4.1 a shekarar 2025, da kuma kashi 4.3 a shekarar 2026,”
Rahoton ya ƙara da cewa, “a Najeriya kuma, ana hasashen tattalin arzikin ƙasar zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025-26. Ana kuma hasashen hauhawar farashin kayayyaki zai ragu,” kamar yadda tashar Channels ta ruwaito daga rahoton.
Haka kuma rahoton ya ƙara da cewa man fetur da ƙasar ke samarwa zai ƙaru a tsakankanin lokacin da ake hasashen haɓakar tattalin arzikin ƙasar, amma duk da haka ba zai kai asalin abin da OPEC ta yi hasashen ƙasar za ta riƙa samarwa ba. In ji BBC.