fidelitybank

TASHIN HANKALI: An kama samari 3 su na dafa kan wata budurwa domin yin asirin samun kuɗi

Date:

An samu gagarumin tashin hankali a yankin Oke Aregba da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, bayan da aka kama wasu samari su na dafa kan wata budurwa da aka ce budurwar ɗaya da ga cikinsu ce, domin yin asirin samun kudi.
A cewar rahoton Daily Post, da sanyin safiyar yau Asabar ne, wani mai suna Segun Adewusi, wanda shi jami’in tsaron al’umma ne, ya lura da yadda wasu yara maza huɗu su ke dafa wani abu da ake zargin kan mutum ne a wata tukunyar a gefen hanya.
Rahotanni sun baiyana cewa, nan take mai gadin ya sanar da ‘yan sandan da ke ofishin Adatan, inda suka je wurin da lamarin ya faru domin kama masu dafa kan, inda su ka cafke uku daga cikin yaran, ɗayan kuma ya tsere kafin ƴan sanda su zo wajen.
Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce yarinyar da aka kashe mai suna Rofiat, mazauniyar Idi-Ape ce; ta kasance budurwa ga wani Soliu, wanda yanzu haka ya na komar ƴan sanda.
An ce Soliu ya yaudari yarinyar ne zuwa ɗakinsa, inda ya riƙe ta ya kuma buƙaci ɗaya da ga cikin abokansa ya yanka ta da wuka.
“Wadanda aka kama sun hada da Wriz Oladeinde mai shekaru 17 daga Kugba, Gafar Luukman mai shekaru 19 daga Kugba da Mustakeem Balogun daga Bode Olude, dukkansu a Abeokuta. Soliu shine saurayin yarinyar, ya gudu, amma daga baya aka kama shi.
“Sun kashe Rofiat, suka yanke mata kai, suka tattara gawar mara kai a cikin buhu sannan suka fara kona kan a tukunya. Sun gaya wa ’yan sanda a gaban taron jama’a cewa suna so su yi amfani da shi wajen asirin samun kuɗi.
“’Yan sanda sun tafi da gawar zuwa dakin ajiyar gawa,” wata majiya ta shaida wa wakilinmu ranar Asabar.
A cikin wani ikirari na faifan bidiyo, Mustakeem Balogun, ya ce, “Mun so mu yi amfani da kanta ne kawai don yin ibadar kudi. Soliu ya shake ta, ya ce in taimake shi, muka yanke mata kai.”
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp