fidelitybank

TASHIN HANKALI: An kama samari 3 su na dafa kan wata budurwa domin yin asirin samun kuɗi

Date:

An samu gagarumin tashin hankali a yankin Oke Aregba da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, bayan da aka kama wasu samari su na dafa kan wata budurwa da aka ce budurwar ɗaya da ga cikinsu ce, domin yin asirin samun kudi.
A cewar rahoton Daily Post, da sanyin safiyar yau Asabar ne, wani mai suna Segun Adewusi, wanda shi jami’in tsaron al’umma ne, ya lura da yadda wasu yara maza huɗu su ke dafa wani abu da ake zargin kan mutum ne a wata tukunyar a gefen hanya.
Rahotanni sun baiyana cewa, nan take mai gadin ya sanar da ‘yan sandan da ke ofishin Adatan, inda suka je wurin da lamarin ya faru domin kama masu dafa kan, inda su ka cafke uku daga cikin yaran, ɗayan kuma ya tsere kafin ƴan sanda su zo wajen.
Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce yarinyar da aka kashe mai suna Rofiat, mazauniyar Idi-Ape ce; ta kasance budurwa ga wani Soliu, wanda yanzu haka ya na komar ƴan sanda.
An ce Soliu ya yaudari yarinyar ne zuwa ɗakinsa, inda ya riƙe ta ya kuma buƙaci ɗaya da ga cikin abokansa ya yanka ta da wuka.
“Wadanda aka kama sun hada da Wriz Oladeinde mai shekaru 17 daga Kugba, Gafar Luukman mai shekaru 19 daga Kugba da Mustakeem Balogun daga Bode Olude, dukkansu a Abeokuta. Soliu shine saurayin yarinyar, ya gudu, amma daga baya aka kama shi.
“Sun kashe Rofiat, suka yanke mata kai, suka tattara gawar mara kai a cikin buhu sannan suka fara kona kan a tukunya. Sun gaya wa ’yan sanda a gaban taron jama’a cewa suna so su yi amfani da shi wajen asirin samun kuɗi.
“’Yan sanda sun tafi da gawar zuwa dakin ajiyar gawa,” wata majiya ta shaida wa wakilinmu ranar Asabar.
A cikin wani ikirari na faifan bidiyo, Mustakeem Balogun, ya ce, “Mun so mu yi amfani da kanta ne kawai don yin ibadar kudi. Soliu ya shake ta, ya ce in taimake shi, muka yanke mata kai.”
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp