fidelitybank

TASHIN HANKALI: An kama samari 3 su na dafa kan wata budurwa domin yin asirin samun kuɗi

Date:

An samu gagarumin tashin hankali a yankin Oke Aregba da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, bayan da aka kama wasu samari su na dafa kan wata budurwa da aka ce budurwar ɗaya da ga cikinsu ce, domin yin asirin samun kudi.
A cewar rahoton Daily Post, da sanyin safiyar yau Asabar ne, wani mai suna Segun Adewusi, wanda shi jami’in tsaron al’umma ne, ya lura da yadda wasu yara maza huɗu su ke dafa wani abu da ake zargin kan mutum ne a wata tukunyar a gefen hanya.
Rahotanni sun baiyana cewa, nan take mai gadin ya sanar da ‘yan sandan da ke ofishin Adatan, inda suka je wurin da lamarin ya faru domin kama masu dafa kan, inda su ka cafke uku daga cikin yaran, ɗayan kuma ya tsere kafin ƴan sanda su zo wajen.
Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce yarinyar da aka kashe mai suna Rofiat, mazauniyar Idi-Ape ce; ta kasance budurwa ga wani Soliu, wanda yanzu haka ya na komar ƴan sanda.
An ce Soliu ya yaudari yarinyar ne zuwa ɗakinsa, inda ya riƙe ta ya kuma buƙaci ɗaya da ga cikin abokansa ya yanka ta da wuka.
“Wadanda aka kama sun hada da Wriz Oladeinde mai shekaru 17 daga Kugba, Gafar Luukman mai shekaru 19 daga Kugba da Mustakeem Balogun daga Bode Olude, dukkansu a Abeokuta. Soliu shine saurayin yarinyar, ya gudu, amma daga baya aka kama shi.
“Sun kashe Rofiat, suka yanke mata kai, suka tattara gawar mara kai a cikin buhu sannan suka fara kona kan a tukunya. Sun gaya wa ’yan sanda a gaban taron jama’a cewa suna so su yi amfani da shi wajen asirin samun kuɗi.
“’Yan sanda sun tafi da gawar zuwa dakin ajiyar gawa,” wata majiya ta shaida wa wakilinmu ranar Asabar.
A cikin wani ikirari na faifan bidiyo, Mustakeem Balogun, ya ce, “Mun so mu yi amfani da kanta ne kawai don yin ibadar kudi. Soliu ya shake ta, ya ce in taimake shi, muka yanke mata kai.”
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp