fidelitybank

Tagwaye sun yi wa ƴar shekara 10 fyaɗe a Anambra

Date:

A na zargin wasu ƴan tagwaye, ƴan shekara 16 da haihuwa, Chukwuemeka da Chukwuebuka Okpe, da yiwa wata ƴar shekara 10 fyaɗe na taron dangi a Abagana, Ƙaramar Hukumar Njikoka ta Jihar Anambra.
Babbar Daraktar Gidauniyar Davina Care Foundation, Rachel Yohanna, ita ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Lahadi, a Awka, cewa mahaifiyar yarinyar, Benedict Sunday, wacce ma’aikaciyar jinya ce,  ta kawo karar.
NAN ta samu labarin cewa waɗanda ake zargin ƴaƴan mai kula da gidan da yarinyar ta ke zaune da iyayenta ne inda a ka ce ƴan tagwayen sun ci gaba da cin zarafin ta sabo da taki yarda da su yi mata fyaɗe a karo na biyu.
Yohanna ta ce an kai rahoton laifin a ofishin ‘yan sanda na Abagana a ranar 16 ga watan Janairu, kuma an kama wadanda ake zargin da mahaifiyarsu, Chinwe Okpe.
Ta ce an kai yarinyar zuwa cibiyar binciken laifukan fyaɗe ta Ntasi da ke babban asibitin Enugu-Ukwu, inda aka tabbatar da cewa an ci zarafin ta kamar yadda wasu gurare a gabanta da bayanta su ka nuna.
Ta kuma ce an kai yarinyar, tare da rakiyar dan sanda da wata innar ta zuwa gwaji na biyu a asibitin ‘yan sanda, yayin da mahaifiyar wadanda ake zargin ta ce sakamakon asibitin Ntasi na jabu ne.
A cewar Yohanna, da sakamakon gwaji na biyun ya fito, sai ya nuna cewa lallai an yi wa yarinyar fyaɗe.
 Yohanna ta ce a lokacin da ‘yan sanda ke yi mata tambayoyi, wadda abin ya shafa ta ce ‘yan tagwayen ne suka kai mata hari a bandaki yayin da mahaifiyarta ba ta nan, suka kwantar da ita a ƙasa su ka kuma yi mata fyaɗe.
“Yaran tagwayen har yanzu suna musanta cewa sun yi wa yarinyar fyaɗe,” in ji ta.
Yohanna ta ce yanzu haka yarinyar na ƙarƙashin kulawa yayin da aka mika karar zuwa sashin binciken manyan laifuka da leken asiri na  Akwa, domin ci gaba da bincike.
Ta ce za a gurfanar da tagwayen a gaban kotun shari’ar iyalai bayan bincike, yayin da gidauniyar za ta tattara tallafi da bin diddigin lamarin don tabbatar da cewa yarinyar ta samu taimakon jinya da kuma adalci,” inji ta.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp