fidelitybank

Tagwaye sun yi wa ƴar shekara 10 fyaɗe a Anambra

Date:

A na zargin wasu ƴan tagwaye, ƴan shekara 16 da haihuwa, Chukwuemeka da Chukwuebuka Okpe, da yiwa wata ƴar shekara 10 fyaɗe na taron dangi a Abagana, Ƙaramar Hukumar Njikoka ta Jihar Anambra.
Babbar Daraktar Gidauniyar Davina Care Foundation, Rachel Yohanna, ita ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Lahadi, a Awka, cewa mahaifiyar yarinyar, Benedict Sunday, wacce ma’aikaciyar jinya ce,  ta kawo karar.
NAN ta samu labarin cewa waɗanda ake zargin ƴaƴan mai kula da gidan da yarinyar ta ke zaune da iyayenta ne inda a ka ce ƴan tagwayen sun ci gaba da cin zarafin ta sabo da taki yarda da su yi mata fyaɗe a karo na biyu.
Yohanna ta ce an kai rahoton laifin a ofishin ‘yan sanda na Abagana a ranar 16 ga watan Janairu, kuma an kama wadanda ake zargin da mahaifiyarsu, Chinwe Okpe.
Ta ce an kai yarinyar zuwa cibiyar binciken laifukan fyaɗe ta Ntasi da ke babban asibitin Enugu-Ukwu, inda aka tabbatar da cewa an ci zarafin ta kamar yadda wasu gurare a gabanta da bayanta su ka nuna.
Ta kuma ce an kai yarinyar, tare da rakiyar dan sanda da wata innar ta zuwa gwaji na biyu a asibitin ‘yan sanda, yayin da mahaifiyar wadanda ake zargin ta ce sakamakon asibitin Ntasi na jabu ne.
A cewar Yohanna, da sakamakon gwaji na biyun ya fito, sai ya nuna cewa lallai an yi wa yarinyar fyaɗe.
 Yohanna ta ce a lokacin da ‘yan sanda ke yi mata tambayoyi, wadda abin ya shafa ta ce ‘yan tagwayen ne suka kai mata hari a bandaki yayin da mahaifiyarta ba ta nan, suka kwantar da ita a ƙasa su ka kuma yi mata fyaɗe.
“Yaran tagwayen har yanzu suna musanta cewa sun yi wa yarinyar fyaɗe,” in ji ta.
Yohanna ta ce yanzu haka yarinyar na ƙarƙashin kulawa yayin da aka mika karar zuwa sashin binciken manyan laifuka da leken asiri na  Akwa, domin ci gaba da bincike.
Ta ce za a gurfanar da tagwayen a gaban kotun shari’ar iyalai bayan bincike, yayin da gidauniyar za ta tattara tallafi da bin diddigin lamarin don tabbatar da cewa yarinyar ta samu taimakon jinya da kuma adalci,” inji ta.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp