Gwamna jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya mika sakon ta’aziyar sa ga iyalan marigayi, Alhaji Bashir Othman Tofa, bisa rasuwa da ya yi a safiyar ranar Litinin.
A wata sanarwa dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba, gwamnan ya bayyana irin sadaukarwar da Tofa ya yi, wanda ya fara daukar nauyin jagoranci tun ya na karami, a lokacin da a ka zabe shi kansila a Tofa ya na dan shekara 20, kuma ya ci gaba da kasancewa mai hidima da kuzari a al’amuran sa, har zuwa lokacin mutuwarsa.
Ya ce”A matsayinsa na dan kasuwa, kuma mai taimakon jama’a, Tofa ya taba rayuwar mutane da dama, kuma imanin cewa, abubuwan da ya bari a baya za su yi tasiri kusan zuriya baki daya, nasarorin da ya samu a siyasance za su kasance muhimman bayanai a cikin adabin gwamnatin Najeriya da kuma siyasar da za su ci gaba da zuwa”.
Sanarwar ta kara da cewa, “Ya kasance babban mutum, dan dimokradiyya kuma fitaccen dan siyasa wanda ya bar rubuce-rubucen siyasa da tarihin siyasar Najeriya,” in ji sanarwar.
Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikan sa da Aljannar Firdausi da kuma ‘yan uwa da abokan arziki da kuma abokan arziki ya jikan wannan rashi mara misaltuwa.