fidelitybank

Ta’aziyya: Murtala Garo ya jagoranci shugabannin hukumomi zuwa wajen Kwankwaso

Date:

Kwamishinan kananan hukumomi na Jihar Kano, Hon. Murtala Sule Garo, ya jagoranci shugabannin kananan hukumomi 44 na jihar a ziyarar ta’aziyyar Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, bisa rasuwar kanin sa, Inuwa Kwankwaso.

Kwamishinan da shugabannin kananan hukumomin, wadanda su ka nuna alhininsu game da rasuwar Inuwa, sun yi addu’ar Allah ya jikan marigayin.

PlatinumPost ta rahoto cewa a baya Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya kai ziyara ga Kwankwaso, inda ya jajanta wa tsohon gwamnan a madadin gwamnatin jihar da kuma al’ummar jihar.

Inuwa, wanda kani ne ga Sanata Kwankwaso ya rasu ne a safiyar ranar Litinin 20 ga watan Disamba, 2021 a asibitin koyarwa na Aminu Kano bayan doguwar jinya ya na da shekaru 64.

Ya kasance ma’aikacin gwamnati mai ritaya kuma injiniyan noma. Marigayin ya bar matarsa da ‘ya’ya mata biyu: Barr. Nafisa Inuwa da Zainab Inuwa.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp