fidelitybank

Ta’addanci: Sojoji sun ragargaji yaran Turji a Sokoto

Date:

Rundunar Sojojin kasar nan sun kashe ’yan ta’adda da dama a musayar wuta da su ka yi da yaran dan bindigar nan, Bello Turji a Jihar Sokoto.

Yaran na Bello Turji sun gamu da ajalinsu ne a kauyukan Katanga da Satiru, bayan Babban da Kwamanda (GOC) na Runduna ta 8 ta Sojin kasa ta Najeriya ya jagoranci sojoji su ka shiga har kauyukan sun yi musu kofar rago a ranar Alhamis.

Aminiya ta rawaito cewa, wani dan sa-kai da ke tare da sojoji a lokacin harin ya ce, “A akalla motoci 20 ne su ka yi wa wurin dirar mikiya, mun dauki awanni mu na musayar wuta da su; In takaita maka bayani, har sai da jirgin yaki ya kawo dauki mu ka fatattake su suka ja baya. Zuwa yanzu da wuya a iya tantance yawan wadanda mu ka kashe, amma ba a kashe mana ko mutum daya ba. Mun samu nasara”.

Bayanan da Aminiya ta samu sun nuna cewa baya kauyukan Katanga da Satiru na hanun Turji da yaransa, suna cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin, Isa ya shaida cewa, a lokacin da a ke ba-ta-kashin, sun ga dandazon ’yan bindiga na zuwa wurin, domin marawa ’yan uwansu baya.

“Amma bayanan da muka samu sun nuna sun kwashi kashinsu a hannun sojoji; Yanzu haka GOC da dakarunsa na bin daji suna share ’yan bindigar a maboyansu”. A cewarsa.

Wata majiyar soji ta ce GOC din ya lashi takobi cewa ba zai kowa gida ba sai sun gama fatattakar ’yan bindiga daga yankin Gabashin Jihar Sakkwato.

“Jajirtacce ne kuma ba ya son duk abin da zai kawo nakasu, shi da kan shi ya ke jagorantar sojoji a daji,” inji majiyar.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp