Kungiyar kwallon kafa ta Abubakar Rimi Television (ARTV) Kano, sun samu nasara a wasan su na farko na gasar cin kofin kungiyar marubuta labarin wasanni ta ƙasa reshen jihar Kano (SWAN), bayan da suka lallasa Radio Nigeria (Pyramid FM) da ci ɗaya da nema.
Ɗan wasan ARTV, Aliyu Ibrahim ne ya zura ƙwallo tilo a ragar Pyramid a minti 50, wanda ya baiwa ARTV samun nasara a gasar.
Bayan an tashi wasan mai ban sha’awa, kungiyoyin biyu sun kasa zura kwallo a raga duk da damammakin cin kwallo da suka samu, wanda ARTV ta na saman rukunin B da maki 3.
Wasan wanda ya gudana a filin wasa na Kano Pillars, Sabon Gari ya samu halartar dimbin magoya bayan da manyan baki da suka hada da shugaban hukumar wasanni ta Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Galadima, Darakta Janar ta gidan Talabijin na Abubakar Rimi (ARTV), Hajiya Sa’a Ibrahim da Alhaji Dr. Danburam Abubakar Nuhu da sauran jama’a.
Za a ci gaba da wasannin gobe Asabar 4 ga Disamba 2021 tare da wasanni uku a rukunin A da B.