Akalla mutane hudu ne suka mutu, yayin da wasu suka jikata a wani hari da aka kai kauyukan Dugara da Daurawa da kuma Gidan Gadi, duka a karamar hukumar Matazu da ke jihar Katsina.
Mazauna yankin sun shaidawa manema labarai cewa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 na daren Juma’a.
Wani mazaunin kauyen ‘Yarkirya, Usman Ibrahim, ya ce ‘yan ta’addan sun mamaye kauyukan da muggan makamai tare da lalata gidaje da dama yayin hare-haren.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a Katsina, ya ce, ba su da labarin kai harin.
Ya ce hakan na iya faruwa ne sakamakon rashin sadarwa a yankin da lamarin ya faru.
Isah ya bada tabbacin zai yi wa jama’a bayanin gaskiya ko akasin haka da zarar ya tabbatar da faruwar lamarin.