Najeriya ta lallasa Sudan da ci 3-1 a gasar cin kofin AFCON 2021 bayan sun kara a filin wasa na Stade Roumdé Adjia da ke Garoua na kasar Kamaru ranar Asabar.
Nasarar ta baiwa Super Eagles tabbacin samun gurbin zuwa zagaye na 16.
Da wannan nasara Super Eagles ta samu nasara a wasanni biyu na farko a gasar cin kofin Afrika a gasar da ta buga a jere a karon farko, a cewar hukumar kwallon kafar Afirka.
Walieldin Khedr na Sudan ne ya zura kwallo a bugun fenareti a minti na 70 da fara wasa inda Najeriya ta ci 3-1.
Ola Aina ya yi wa dan wasan Sudan keta ne lokacin da VAR ta ba Falcons bugun daga kai sai mai tsaron gida. An bai wa dan wasan baya na Najeriya katin gargadi.
Kwallon da Samuel Chukwueze ya ci ne ta saka Najeriya a gaba a minti uku da fara wasa ta hannun Moses Simon. Taiwo Awoniyi ya zura kwallo a minti 45 sai kwallon Samuel Chikwueze da ya fara zura kwallon farko a minti 3.
Najeriya za ta kara wasan ta na 3 a ranar Laraba 19 ga wata tare da Guine Bissau.