Rundunar sojoji ta kashe ‘yan fashin daji 11 a lokacin wata arangama da ‘yan fashin a yankin ƙaramar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.
A wata sanarwa da kwamishin tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan, ya fitar ya ce a lokacin gumurzun dakarun sun yi arangama da ‘yan fashin dajin a ƙauyen Kakangi da katakaki.
Sanarwar ta ce, dakarun sun lalata sansanonin ‘yan fashin a garuruwan Bagoma da Rema da Bugai da Dagara da Sabon layi da Gagumi da Kakangi da katakaki da kuma Randagi.
Karanta Wannan: Ƴan bindiga sun sace mata biyu a jami’ar Tarayya ta Gusau
Aruwan ya ce, sojojin sun samu nasarar kashe ‘yan fashi 11 yayin da wasu da dama suka tsere da raunukan harbin bindiga.
Haka kuma sanarwar ta yi bayanin cewa a lokacin arangamar sojojin sun samu nasarar ƙwato bindigogi biyu ƙirar AK-47, da kwanson alburusan bindigogin biyu, sai alburusai 57 da babura shida.
Gwamnan jihar Malam Nasir El-rufai ya jinjina wa sojojin bisa wannan nasara, tare da kiransu da su ƙara ƙaimi wajen samun nasarar fatattakar ‘yan fashin daji a faɗin jihar.