fidelitybank

Sojoji sun kashe kasurgumin dan bindigan Kaduna

Date:

Rundunar Sojojin Saman Kasar nan. ta sanar da cewa ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Mustapha Abdullahi, da wasu yaransa guda biyar a Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Arewa na Jihar Kaduna.

Daraktan watsa labarai da hulɗa da jama’a na rundurar, Edward Gabkwet ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce ɓangaren sojojin rundunar na musamman na 413 ne suka yi aikin.

Mista Gabkwet ya ce an tura sojojin ne bayan samun bayanan sirri a ranar 31 ga Agustan cewa ɗan bindigar tare da yaransa sun tunkari dajin Sabon Gida da ke kan hanyar Sabon Birni, inda ake tunanin sun nufa da zimmar garkuwa da mutane, ko cutarwar da wasu ko kashewa.

A cewarsa, ganin sojojin ke da wuya, sai ƴan bindigar suka buɗe wuta, wanda hakan ya sa sojojin suka mayar da martani har suka ci ƙarfinsu.

Sojojin sun samu nasarar kashe jagoran ƴan bindigar da yaransa, inda aka ƙwato bindigogin ƙirar gida da alburusai da wayoyoyi da layukan waya da sauransu.

“Muna cigaba da ƙoƙarin ganin mun fatattaki ƴan bindiga daga yankin Igabi da Birnin Gwari baki ɗaya.

“An kuma yaba wa ƙoƙarin sojojin tare da kira a gare su da ƙara ƙaimi a wannan aiki da suke yi na kare rayuwa da dukiyar al.umma,” inji shi.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp